Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2009-10-20 21:34:13    
Za'a bude dandalin tattaunawa kan bunkasuwa da hadin-gwiwar Sin da Afirka ta fannin masana'antu na shekara ta 2009 a Beijing

cri
Ranar 20 ga wata, a nan birnin Beijing, babban magatakardan kungiyar kula da harkokin hadin-gwiwa ta fannin masana'antu ta kasar Sin Mista Zheng Boliang ya bayyana cewa, za'a kaddamar da "dandalin tattaunawa kan neman bunkasuwa da hadin-gwiwar Sin da Afirka ta fannin masana'antu na shekara ta 2009" a ranar 21 ga watan Nuwamba a nan birnin Beijing, lamarin da zai samar da wani sabon dandali ga hadin-gwiwar Sin da Afirka ta fannonin tattalin arziki da cinikayya.

Mista Zheng ya ce, makasudin shirya wannan dandalin tattaunawa shi ne, a ci gaba da inganta dangantakar abokantaka ta hadin-gwiwa bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Afirka, da karfafa hadin-gwiwar bangarorin biyu wajen zuba jari da yin mu'amala ta fannin masana'antu.

Bisa labarin da muka samu, an ce, babban taken dandalin tattaunawa a wannan gami shi ne, "nuna amincewar juna da neman cimma moriyar juna", haka kuma dandalin tattaunawar zai samu halartar ministocin masana'antu da wakilan kamfanoni daban-daban da zasu zo daga kasashen Afirka sama da 40.(Murtala)