Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-07-03 19:01:47    
Ko-ta-yaya Sin ba za ta amince da a saka batun siyasa a gasar wasannin Olympics ba

cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Liu Jianchao ya bayyana yau 3 ga wata a nan birnin Beijing cewar, ko-ta-kaka bangaren Sin ba zai amince da a saka batun siyasa a gasar wasannin Olympics ba. Ya ce, duk wani yunkurin saka batun siyasa a gasar wasannin Olympics, da yin shiga-sharo-ba-shanu cikin harkokin gidan kasar Sin zai ci tura!

A wajen taron manema labaru da ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta shirya a wannan rana, wani dan jarida ya yi tambaya cewa, akwai kasashe kalilan wadanda suka saka batun siyasa a cikin gasar wasannin Olympics. To, menene ra'ayin bangaren Sin dangane da wannan lamari?

Liu Jianchao ya amsa cewar, bisa ra'ayin "Tsarin Mulkin Olympics", bai kamata ba a saka batun siyasa cikin gasar wasannin Olympics, ya kamata daukacin kasashe membobin gasar wasannin Olympics su mutunta wannan ra'ayi. Ko-ta-yaya bangaren Sin ba zai amince da a saka batun siyasa a gasar wasannin Olympics ba!(Murtala)