Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-06-04 16:18:02    
Kasar Sin ta bayar da babbar ka'idar tsugunar da marayu da tsoffi da nakasassu da iyalansu suka mutu cikin bala'in girgizar kasa na Sichuan

cri
A kwanan baya, ma'aikatar kula da harkokin jama'a ta kasar Sin ta bayar da babbar ka'idar tsugunar da marayu da tsoffi da nakasassu da dukkan iyalansu suka mutu a cikin bala'in girgizar kasa da ya auku a gundumar Wenchuan ta lardin Sichuan.

Game da yaran da har yanzu ba a dauke su ba tukuna, bisa ka'idar da aka bayar, an ce, da farko dai a yi namijin kokarin neman iyayensu da iyalansu. Sannan kuma a tsugunar da su a cikin gidajen jin kai da makarantun gwamnati da suke da sharuda masu kyau. Idan akwai matsalar tsugunar da su a lardin Sichuan, ma'aikatar kula da harkokin jama'a ta kasar Sin za ta daidaita aikin tsugunar da su. Bayan da aka tabbatar da asalin marayu, za a dauki hanyoyi iri daban daban na tsugunar da su. Musamman ne an nuna cewa, lokacin da ake tsugunar da marayun da suka kai fiye da shekaru 10 da haihuwa a sauran gidaje, dole ne a nemi amincewa daga marayu. (Sanusi Chen)