A ran 8 ga wata, za a fara yawo da fitilar wasannin Olympics a birnin Shenzhen da ke lardin Guangdong na kasar Sin, wanda ya kasance yankin musamman na tattalin arziki na farko a kasar Sin. Bisa labarin da jami'in ofishin watsa labarai na gwamnatin Shenzhen ta bayar a yau 7 ga wata, an ce, za a ratsa shahararrun wurare da dama a birnin Shenzhen a yayin da ake yawo da fitilar, wadanda suka nuna nasarorin da aka cimma a birnin Shenzhen a yayin da ake bude kofa ga kasashen waje da yin gyare-gyare a gida a cikin shekaru 30 da suka wuce. Bayan haka, an riga an tabbatar da dukan mutanen da za su yi yawo da fitilar a birnin Shenzhen.
An ce, za a fara yawo da fitilar wasannin Olympics a gobe da safe, da misalin karfe 8, kuma tsawon hanyar da za a bi zai kai kilomita 41.6, kuma daga daya mutane 208 za su yi yawo da fitilar.(Lubabatu)
|