Bisa gayyatar da gwamnatin kasar Japan ta yi masa ne, Mr Hu Jintao, shugaban kasar Sin ya sauka birnin Tokyo a yau Talata don fara yin ziyarar aiki a kasar Japan, wato ziyarar kwanaki biyar a yanayin bazara.
Wannan ziyarar da wani shugaban kasar Sin ya sake yi wa kasar Japan bayan shekaru 10 da suka wuce.
Bayan da ya sauka a filin jirgin sama mai suna Haneda na kasar Japan, Mr Hu Hintao ya bayar da jawabi a rubuce cewa, shekarar nan shekara ta 30 ce da aka daddale yarjejeniyar zaman lafiya da aminci a tsakanin Sin da Japan. Ya kasance da sabuwar dama wajen kara yalwata hulda a tsakanin kasashen biyu. Ya kara da cewa, yana fatan za a kara amincewa da juna, da kara dankon aminci, da inganta hadin gwiwa, da tsara makoma ta hanyar wannan ziyara, ta yadda za a bude wani sabon shafi ga yalwata dangantakar moriyar juna a tsakanin Sin da Japan daga manyan tsare-tsare. Ya yi imani cewa, bisa kokarin da kasashen biyu ke yi tare, tabbas ne, ziyarar za ta cim ma manufar da aka tsara.
A ranar da ya sauka a birnin Tokyo, Mr Hu Jintao ya gana da dangi da zuriyar baya na aminanmu da dama na kasar Japan wadanda suka taba ba da babban taimako wajen kulla huldar diplomasiya a tsakanin Sin da Japan. (Halilu)
|