Yau da asuba, tocilan wasannin Olympics na Beijing ya sauka a birnin Nagano na Japan, wato zango na 16.
Jakadan kasar Sin dake wakilci a kasar Japan Mr. Cui Tiankai ya jagoranci dukkan ma'aikatar ofishin jakadancin zuwa filin jirgin sama don taryen tocilan, inda ya furta cewa, a shirye muke wajen yin yawo da tocilan gobe Asabar a birnin Nagano. Ina cike da kyakkyawan fatan samun nasarar zagayawa da tocilan na wasannin.
An labarta cewa, yau da maraice, kwamitin zartarwa mai kula da harkokin yawo da tocilan na wasannin Olympics na Beijing ya gudanar da wani taro domin bada karin haske ga masu dauke da tocilan. ( Sani Wang )
|