" Wajibi ne a bada tabbaci ga yin yawo da fitilar wasannin Olympics na Beijing a birnin Ho Chi Minh na Vietnam lami-lafiya, kamar yadda firaministan kasar Nguyen Tan Dung ya bayyana a ranar jiya Lahadi.
Sa'annan Mr. Nguye Tan Dung ya furta cewa, ko da yake a yanzu haka ya kasance da kyakkyawan yanayin tsaro a zamantakewar al'ummar Vietnam, amma wassu mutane suna gayyar kokari har kullum wajen tauye irin wannan zaman karko da kuma lahanta kwarjini da kuma matsayin Vietnam a dandalin kasashen duniya. Daga bisani, ya bukaci gwamnatin birnin Ho Chi Minh da ta yin hadin gwiwa sosai tare da sassan da abin ya shafa don yin yawo da fitilar wasannin Olympics lami-lafiya, ta yadda hakan zai bayyana kaunar da jama'ar Vietnam ke nuna wa wasannin motsa jiki da zaman lafiya da kuma zumunci irin na musamman daketsakanin kasashen Vietnam da Sin. ( Sani Wang )
|