A kwanakin baya, bi da bi ne Malamai da dalibai na jami'an wurare dabam daban na kasar Sin suka nuna cewa, ya kamata a nuna kishin kasa ta hanyar da ya kamata, kada a nuna adawa ga "saka batun siyasa a gasar wasannin Olympics" ta hanyar siyasa.
Daliba Shao Yan ta jami'ar Nanchang da abokan karatunta da yawa sun sa hannu kan shafin yanar gizo ta Internet domin nuna goyon baya ga ayyukan mika wutar yola ta wasannin Olympics na Beijing. Ta ce, ya zuwa yanzu, kasar Sin tana fuskantar hali mai tsanani a duniya yayin da take neman bunkasuwa. Ya kamata mu huce, musamman ma a wannan lokaci.
Mr. Gui Yifan shugaban jami'ar horar malamai na Jiangxi yana ganin cewa, idan an kwatanta da yawancin 'yan siyasa da jama'a na kasashen duniya suke nuna zumunci ga kasar Sin da goyon bayan wasannin Olympics na Beijing, da mutanen kasashen duniya masu adawa da kasar Sin tsiraru ne. Ya kamata mu daidaita wannan matsala da basira, bai kamata mu dauki da ba su dace ba.
Mr. Zhao Wanwei daliba ta jami'ar Beijing ta ce, matasa masu kishin kasa na kasar Sin su tinkari rikici iri iri yadda ya kamata, su nuna adawa ga"saka batun siyasa a gasar wasannin Olympics"ta hanyar siyasa.
|