Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-04-18 14:07:18    
Sinawa mazaunan kasashen waje a kasar Amurka suna ta nuna rashin jin dadi ga abin da Dalai Lama ke yi

cri
A ran 16 ga wata, Sinawa mazaunan kasashen waje dake jihar Minnesota na kasar Amurka sun yi zanga-zanga don nuna rashin jin dadi ga yunkurin neman 'yancin kan Tibet da Dalai Lama ke yi a wurin, da kuma fallasa abin da Dalai ke yi na zuga masu neman yancin kan Tibet da su lallata gasar wasannin Olympic na Beijing.

Bisa labarin da kanfanonin watsa labaru a wurin suka bayar, an ce, ran nan da safa, Sinawa mazaunan kasashen waje dake jihar Minnesota sama da 50 sun daga tutar kasar Sin da allunan kirari sun yi zanga-zanga a titin birnin Rochester. Sinawa da suka shiga zanga-zangar sun gaya wa kanfanonin watsa labaru cewa, sun ji fushi sosai sabo da yada jita-jita da Dalai Lama ke yi kan tarzoma dake auku a jihar Tibet, sa'I daya kuma, ba su son wadansu 'yan siyasa na Amurka da su sa hannu a cikin harkokin gida na kasar Sin.

A ran 15 ga wata kuma, Sinawa mazaunan kasashen waje da daliban kasar Sin dake birnin Seattle sun shiga zanga-zanga don shimfida zaman lafiya da aka shirya a filin wasan kwalon kwando a jami'ar Washington, don nuna rashin jin dadi ga yunkurin neman yancin kan Tibet da Dalai ke yi.

Mr. Tan Wenzhao, daya daga cikin mutane masu shiryar zanga-zangar nan ya bayyana cewa, Sinawa mazaunan kasashen waje da daliban kasar Sin dake kasashen waje sun shirya zanga-zangar da kansu ta Internet, don metanen kasar Amurka sun iya kara fahimtar abin gaskiya game da tarzoma da ta auku a jihar Tibet na kasar Sin. (Zubairu)