Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-04-08 20:25:00    
Kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin ta musanta maganar da Dalai Lama ya yi ta cewar, wai yana tsayawa kan "Tsakiyar hanya"

cri
A gun taron manema labaru da aka shirya a yau 8 ga wata a nan birnin Beijing, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin madam Jiang Yu ta musanta maganar da Dalai Lama ya yi a kwanan baya a "Takardar gaya wa 'yan uwa na Tibet", inda ya bayyana cewa, ba ya da nufin "neman 'yancin kan Tibet", amma yana tsayawa kan "Tsakiyar hanya". Madam Jiang Yu ta ce, Dalai yana wakiltar tsarin bayi na manoma, wanda ya hada da siyasa da addinai. Babu dimokuradiya, da 'yancin kai, da kuma hakkin bil Adam a karkashin wannan tsari, sai hakkin musamman na masu tafiyar da mulki kawai. Nufin "Tsakiyar hanya" da Dalai Lama ke nema, shi ne, komawa kan tsarin.

A waje daya kuma, madam Jiang Yu ta musanta maganar da Dalai Lama ya yi ta cewar, wai ba ya da nasaba da lamarin duka da kwacewa da kone-kone, wanda ya faru a birnin Lasah. Ta jaddada cewa, abin da Dailai Lama ya yi a kwanan baya shi ne, tayar da shirya lamari na nuna karfin tuwo a birnin Lasah. (Bilkisu)