Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-04-07 20:51:36    
An sake bude kofar wuraren al'adu da nishadi ga jama'a a birnin Lhasa

cri

Tare da komar da oda yadda ya kamata a birnin Lhasa, an sake bude kofar wuraren al'adu da nishadi ga jama'a, wadannan na'urori an rufe su ne sakamakon lamarin da ya faru a ranar 14 ga watan jiya.

Ran 6 ga wata, ranar Asabar, wakilimmu ya shiga cikin dakin nune nune na jihar Tibet, ya ga yawan mutanen da suke ziyara a dakin ya karu zuwa matsayin yadda ya kamata. A dakin littattafai na birnin Lhasa, jama'a suna zaune a gaban tebur, suna karatu cikin kwanciyar hankali. A cikin wani shahararren dakin motsa jiki na birnin Lhasa, wasu 'yan mata suna yin wasan lankwashe jiki. A gabansu kuma, matasa da yawa suna liftin .

Da dare ya yi, jama'ar Tibet sun fara zaman rayuwa da dare kamar yadda suke yi a da.(Danladi)