Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2008-04-07 12:50:55    
Yawan manema labaru da za su zo don neman labaru kan wasannin Olympic na Beijing zai kai dubu 20

cri

Memban kwamitin watsa labaru na kwamitin shirya wasannin Olympic na kasa da kasa kuma mataimakin shugaban kungiyar manema labarun wasanni na kasar Sin Gao Dianmin ya fayyace a ran 6 ga wata a birnin Shanghai dake gabashin kasar Sin cewa, manema labaru dubu 20 za su zo kasar Sin domin neman labarun wasannin Olympic na Beijing, rabinsu wakilan gidajen TV ne da masu ba da tamako gare su. Yawan manema labarun babban yankin kasar Sin zai kai kimanin dari 3.

Gao Dianmin ya bayar da wannan labari ne a yayin da ya ba da lacca a jerin kos din wasannin Olympic a birnin Shanghai cewa, a karo na farko ne kwamitin wasannin Olympic ya sayar da ikon ba da shirye-shiryen wasannin Olympic ta Internet a gun wasannin Olympic na Beijing, tashar internet ta gidan TV ta kasar Sin da wata tashar internet ta Australia sun samu ikon a karshe. Ban da wannan kuma, a gun wasannin Olympic na Beijing, 'yan wasanni sun iya shirya Blog nasu, wannan shi ne karo na farko a cikin tarihin wasannin Olympic.(Lami)