A ran 10 ga wata a birnin Beijing, zaunannen mamban Ofishin siyasa na tsakiya na Jam'iyyar Kwaminis ta Sin kuma jagora na taron tawagar shugabanci na babban taron farko na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta jama'ar kasar Sin ta 11 Mr Jia Qinglin, da kuma zaunannen mamban Ofishin siyasa na tsakiya na Jam'iyyar Kwaminis ta Sin kuma darektan hukumar siyasa da shari'a na kwamitin tsakiya na Jam'iyyar Kwaminis ta Sin Mr Zhou Yongkang suka halarci tattaunawar tawagogin Ningxia da Heilongjiang kan taron farko na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ta 11.
Mr Jia Qinglin ya bayyana cewa, shekarar bana, cikon shekaru 50 ke nan da kafuwar jihar Ningxia ta kabilar Hui mai ikon tafiyar da harkokin kanta, yana fatan jihar Ningxia za ta kyautata hanyar da take bi wajen raya tattalin arziki, da kyautata zaman rayuwar jama'a da kiyaye hadin kan kabilu daban daban, da zaman jituwa a tsakanin addinai daban daban.
Mr Zhou Yongkang ya ce, ya kamata a mai da hankali sosai kan matsalolin da ke jawo hankulan jama'a, da zurfafa yin gyare gyare kan tsarin dokokin shari'a, domin tabbatar da adalci.(Danladi)
|