Yayin da yake hira da wakilin BBC a jiya 14 ga wata, shugaba Bush na kasar Amurka ya bayyana cewa, zai halarci taron wasannin Olympics da za a gudanar a birnin Beijing kamar yadda aka shirya.
Game da hada batun Darfur da wasannin Olympics da za a gudanar a birnin Beijing, har ma nuna adawa da wasannin, da wasu suka yi, Mr.Bush ya ce, zai halarci taron wasannin Olympics, kuma ba zai tattauna batun siyasa bisa wasannin Olympics ba.(Lubabatu)
|