Ran 29 ga wata, ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin ya yi taro domin nazarin aikin shirin wasannin Olympic da wasannin Olympic na nakasassu na Beijing. A gun taro, an jaddada cewa, kasar Sin za ta kara yin hadin gwiwa tare da kungiyar wasannin Olympic na duniya da hukumomin da abin ya shafa domin neman yi wani wasannin Olympic da wasannin Olympic na nasasassu da ke da tsarin musamman da babban matsayi.
A gun taro, ana ganin cewa, wasannin Olympic shi ne fatan jama'a na zaman al'umma dabam daban na kasar Sin, shi ne burin jama'ar kasar Sin a cikin dogon lokacin da ya wuce, kuma shi ne nauyi da aikin da kasar Sin ke daukar ga kasashen duniya.
|