Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-12-11 09:47:15    
Bunkasuwa ta zo a gaban kome a idanun kasashen Afirka

cri

Don tabbatar da samun bunkasuwar kasashen duniya tare, a wannan shekara, kasashe da kungiyoyin duniya da abin ya shafa sun ci gaba da kyautata tsarin bai wa Afirka tallafawa, sun kuma karfafa karfin taimako. Tsarin taron dandalin tattaunawa kan yin hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka ba kawai ya daukaka ci gaban Sin da Afirka a fannoni daban daban ba, har ma ya samar da misali ga sauran kasashe da yankuna domin yin mu'amala da hadin gwiwa da Afirka cikin daidaici. Lin Lin, jakadan kasar Sin a kasar Habasha ya ce,'Tsarin taron dandalin tattaunawa kan yin hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka ya sanya sauran kasashe da yankuna su kara mai da hankulansu kan Afirka. Kasashen Turai sun sami sabon ci gaba a fannin raya hulda a tsakaninsu da kasashen Afirka a shekarun baya. Kasashen Kudancin Amurka kuwa sun kira taron koli na farko a tsakaninsu da Aifkra a birnin Abuja, hedkwatar Nijeriya a karshen shekarar bara. Kasar Sin ta fadakar da su bisa kyakkyawar hulda a tsakaninta da kasashen Afirka. Bugu da kari kuma, sauran kasashen duniya su ma za su mai da hankulansu kan Afirka.'

An yi imani da cewa, saboda kokarin da kasashen Afirka suke yi, da kuma taimakon da kasashen duniya suke bayarwa, tabbas ne kasashen Afirka za su sami karin saurin bunkasuwa.

Kamar yadda El Ghassim Wane, darektan sashen kula da harkokin rikici na kungiyar AU ya fada,'Mun san kalubalen da muke fuskanta. Amma mun yi imani da cewa, Afirka wata nahiya ce da ke da babban boyayyen karfi da ba ta taba amfani da shi ba tukuna, yau da gobe za ta bi hanyar bunkasuwa.'(Tasallah)


1 2