Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-09-10 10:12:19    
Ministan harkokin waje na kasar Sin ya nuna cewa ziyarar Hu Jintao ta samu nasara sosai

cri

Yayin da Yang Jiechi, ministan harkokin waje na kasar Sin ya ke ganawa da 'yan jarida a jirgin sama bisa hanyar dawowarsa daga Australia zuwa kasar Sin a ran 9 ga wata, ya tattara nasarorin da Hu Jintao, shugaban kasar Sin ya samu wajen ziyararsa. Ya nuna cewa, ziyarar nan ta samu nasara, kuma ta jawo hankulan kasashen duniya sosai.

Yang Jiechi ya ce, ziyarar wani mihimmin aiki ne da kasar Sin take fuskanta shiyyar Asiya da tekun Pasific a fannin diplomasiya, kuma ta nuna babbar ma'ana wajen sa kaimi ga bunkasuwar dangantaka tsakanin Sin da Australia da kuma zurfafa hadin gwiwa ta shiyyar Asiya da tekun Pasific. Ya ce, lokacin da Mr Hu ya halarci kwarya-kwaryan taro na 15 na shugabannin kungiyar APEC, shugaba Hu Jintao ya bayyana munafofi da ra'ayoyin da gwamnatin kasar Sin za ta bi a kan muhimmin batun da ke shafar moriyar shiyyoyi da duk duniya.(Zainab)