Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-08-28 21:36:37    
Hu Jintao zai bayyana ra'ayin kasar Sin da kuma matsayin da kasar ke tsayawa a kai dangane da yunkurin hadin gwiwa na Asiya da Pacific

cri
Ranar 28 ga wata a nan birnin Beijing, wani jami'in ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin ya bayyana cewa, a gun kwarya-kwaryar taron shugabanni a karo na 15 na kungiyar hadin gwiwar tattalin arziki ta Asiya da Pacific, wato APEC, wanda za a shirya a nan gaba ba da dadewa ba, shugaba Hu Jintao na kasar Sin zai bayyana ra'ayin kasar Sin da kuma matsayin da kasar ke tsayawa a kai kan yunkurin hadin gwiwa na Asiya da Pacific, da kuma batun magance sauyin yanayi.

Wannan jami'i ya bayyana cewa, kasar Sin na fata za a daddale da bayar da sanarwar Sydney game da sauyin yanayi a gun taron shugabanni, kuma za a zartas da rahoton neman hadin kan tattalin arziki na yankin Asiya da Pacific, bugu da kari kuma za a sa kaimi ga samun sakamako mai kyau tun da wuri wajen shawarwarin kungiyar WTO a zagaye na Doha, da kuma daukaka ci gaban yunkurin gyare-gyaren kungiyar APEC. Ya bayyana cewa, kasar Sin na son yin kokari tare da bangarori daban daban, domin tabbatar da wadannan makasudai. (Bilkisu)