Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-06-29 16:07:40    
Shugaban kasar Sin ya isa Hongkong don halartar bikin murnr cikon shekaru 10 da Sin ta maido da mulkinta a Hongkong

cri

Yau shugaban kasar Sin, Hu Jintao ya isa Hongkong, don halartar bikin murnar cikon shekaru 10 da Sin ta maido da mulkinta a Hongkong da kuma bikin rantsar da sabuwar gwamnatin yankin musamman ta Hongkong.

Gwamnan yankin musamman na Hongkong, Donald Tsang da sauran muhimman jami'an Hongkong tare da jami'an hukumomin gwamnatin tsakiya na kasar Sin da ke Hongkong sun je filin jirgin sama don taryar Hu Jintao da 'yan rakiyarsa.

Ranar 1 ga watan Yuli mai zuwa rana ce ta cikon shekaru 10 da Sin ta maido da mulkinta a Hongkong. A shekaru 10 da suka wuce, gwamnatin kasar Sin ta maido da mulkinta a Hongkong, kuma yankin musamman na Hongkong ya kafu a hukunce.(Lubabatu)