Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-05-23 08:39:42    
Wakilin musamman mai kula da batun Darfur na gwamnatin kasar Sin ya yi ziyara a Darfur

cri
Bisa labarin da muka samu daga kamfanin dillancin labaru na Xinhua, an ce, a ran 22 ga wata Liu Guijin wakilin musamman mai kula da batun Darfur na gwamnatin Sin ya ziyarci shiyyar Darfur dake yammancin kasar Sudan don nazarin halin da ake ciki a Darfur.

Mr.Liu Guijin ya ziyarci El Fashir hedkwatar jihar arewancin Darfur da Nyala hedkwatar jihar kudancin Darfur bi da bi, ya yi rangadi a sansanonin 'yan gudun hujira guda 3 dake wurin, kuma ya sa kafa a kan manyan tituna da kasuwoyi na wannan gari don gane ma idonsa, kuma ya yi hira da mazaunan wurin.

Ban da wannan kuma Mr.Liu Guijin ya zanta da jami'an wurin ciki har da gwamnonin jihohin nan 2 da wakilan bangarori daban daban, ya bayar da jawabi cikin majalisar wakilan jiha da taron maraba da fararen hula suka shirya.

Ya jaddada cewa, gwamnatin kasar Sin tana fatan za a daidaita batun Darfur yadda ya kamata kuma cikin sauri don tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a duk fannoni tun da wuri.(Salamatu)