Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International Saturday    Apr 12th   2025   
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-05-18 08:41:41    
Bankin raya Afirka yana fata kasar Sin za ta kara zuba jari a Afirka

cri

A ran 17 ga wata a birnin Shanghai, shugaban bankin raya Afirka Mr Donald Kaberuka ya bayyana cewa, yana fata kasar Sin za ta kara zuba jari a Afirka.

Mr Kaberuka ya fadi a gun wani taron watsa labaru cewa, yana fata masu zuba jari na kasar Sin da na sauran kasashen duniya za su kara zuba jari a Afirka. Ya ci gaba da cewa, a halin yanzu dai Afirka tana kara samun jari daga kasashen waje, wanda ba a taba ganin irinsa ba a tarihi, wannan yana da kyau ga Afirka. A sa'i daya kuma, Mr Kaberuka yana ganin cewa, Afirka tana bukatar a kara zuba mata jari a fannoni daban daban.

Ban da wannan kuma, Mr Kaberuka yana ganin cewa, babbar matsalar Afirka a fannin muhallin zuba jari ita ce, karancin manyan ayyuka, musamman ma a kan lantarki da dai sauransu albarkatun makamashi. Mr Kaberuka ya ci gaba da cewa, bankin raya Afirka zai kara yin kokari domin kyautata muhallin da ake zuba jari.(Danladi)

© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China. 100040