Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-05-18 08:41:41    
Bankin raya Afirka yana fata kasar Sin za ta kara zuba jari a Afirka

cri

A ran 17 ga wata a birnin Shanghai, shugaban bankin raya Afirka Mr Donald Kaberuka ya bayyana cewa, yana fata kasar Sin za ta kara zuba jari a Afirka.

Mr Kaberuka ya fadi a gun wani taron watsa labaru cewa, yana fata masu zuba jari na kasar Sin da na sauran kasashen duniya za su kara zuba jari a Afirka. Ya ci gaba da cewa, a halin yanzu dai Afirka tana kara samun jari daga kasashen waje, wanda ba a taba ganin irinsa ba a tarihi, wannan yana da kyau ga Afirka. A sa'i daya kuma, Mr Kaberuka yana ganin cewa, Afirka tana bukatar a kara zuba mata jari a fannoni daban daban.

Ban da wannan kuma, Mr Kaberuka yana ganin cewa, babbar matsalar Afirka a fannin muhallin zuba jari ita ce, karancin manyan ayyuka, musamman ma a kan lantarki da dai sauransu albarkatun makamashi. Mr Kaberuka ya ci gaba da cewa, bankin raya Afirka zai kara yin kokari domin kyautata muhallin da ake zuba jari.(Danladi)