Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-04-29 19:51:39    
Mu'ammar al-Qadhafi ya la'anci dakarun da ke adawa da gwamnatin Sudan kan batun shiyyar Darfur

cri

Jiya 28 ga wata, a gun taron ministocin bangarori daban daban da ke shafe batun shiyyar Darfur da aka shirya a birnin Surt da ke gabashin kasar Libyan, shugaban kasar Mu'ammar al-Qadhafi ya la'anci dakarun da ke adawa da gwamnatin Sudan, sabo da suna da nufin mai da batun shiyyar Darfur da ya zama wani batun duniya.

Bisa labarin da muka samu an ce, a lokacin taron, Mr. Al-Qadhafi ya nuna cewa, bai kamata a yarda da ko wane bangaren da ba a amince da shi ba, ya sa baki a batun Darfur, sabo da wannan ya sabawa moriyar kasashen duniya.

Manzon musamman na babban sakataren M.D.D. da ke kula da batun Darfur Jan Eliasson ya bayyana cewa, matsalar shiyyar Darfur wata matsala ce mai tsanani sosai ga kasar Sudan, da duk shiyyar, har ma da duk duniya. Ya jaddada cewa, wannan taro shi ne wata damar da ke iya kara saurin warware matsalar Darfur, da aiwatar da yunkurin tabbatar da zaman lafiya. (Bilkisu)