Firayim ministan kasar Sin Wen Jibao wanda ke yin ziyarar aiki a kasar Korea ta Kudu ya yi shawarwari tare da shugaban kasar Roh Moo-hyun a ran 10 ga wata a fadar Cheongwadae ta shugaban kasar.
Bisa labarin da muka samu, an ce, shugabannin biyu za su yi musanyar ra'ayoyinsu ne kan dangantakar da ke tsakanin kasashen Sin da Korea ta Kudu da kuma al'amuran shiyya-shiyya da kasashen duniya da ke jawo hankulansu. Haka kuma bayan shawarwarin, bangarorin biyu za su rattaba hannu a kan yarjeniyoyi a jere wajen hadin gwiwa tsakaninsu.(Kande Gao)
|