A ran 4 ga wata a birnin Lusaka, hedkwatar kasar Zambiya, shugaban kasar Sin Hu Jintao ya gana da shugaban majalisar dokoki ta kasar Zambiya Amusaa K. Mwanamwambwa da tsohon shugaban kasar Kenneth David Kaunda. A ran nan kuma, kasashen biyu sun bayar da wata sanarwa ciki hadin gwiwarsu, inda suka bayyana cewa, za su kara hadin kansu a fannoni daban daban.
A yayin da yake ganawa da Mr Mwanamwambwa, shugaba Hu ya ce, majalisar wakilan jama'ar kasar Sin da majalisar dokoki ta kasar Zambiya suna da kyakkyawar dangantakar hadin kai a tsakaninsu, kasar Sin tana son kara yin mu'amala da hukumomin kafa dokoki na kasar Zambiya.
A ran nan kuma, bangarorin biyu sun bayar da wata sanarwar tare, inda suka bayyana cewa, bangarorin biyu gaba daya sun yarda da kara yin shawarwari a tsakaninsu da kara hadin kansu, za su kara yin kokari domin ciyar da dangantakar abokantaka a tsakaninsu gaba.(Danladi)
|