Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-02-03 16:22:03    
Hu Jintao ya bar birnin Khartoum bayan da ya gama ziyararsa a kasar Sudan

cri
Bayan da shugaban kasar Sin Hu Jintao ya gama ziyararsa a kasar Sudan, ya tashi daga birnin Khartoum, babban birnin kasar a ran 3 ga wata bisa agogon wurin zuwa kasar Zambia don ci gaba da ziyararsa a kasashen Afirka 8.

Shugaban kasar Sudan Omer El-Bashir ya shirya wani gagarumin baki a filin jirgin sama don yin ban kwana da shugaba Hu da 'yan rakiyarsa.

Lokacin da ya yi ziyara a Sudan, shugaba Hu ya yi shawarwari tare da shugaba El-Bashir, takwaransa na kasar, ban da wannan kuma ya gana da Salva Kiir Mayardit, mataimakin shugaba na farko na kasar da kuma Ali Mohammed Taha, mataimakin shugaban kasar, inda suka yi musanyar ra'ayoyinsu kan dangantakar da ke tsakanin Sin da Sudan da kuma muhimman al'amuran da ke jawo hankulansu. Bugu da kari kuma shugaba Hu ya ziyarci kamfanin sarrafa man fetur na Khartoum wanda kasashen Sin da Sudan suka kafa tare.

Kasar Sudan ita ce zango na uku na wannan ziyarar shugaba Hu a kasashen Afirka 8.(Kande Gao)