A yayin da Mr. Hu Jintao shugaban kasar Sin zai kai ziyarar aiki a kasar Namibiya, jaridar "Southern Times" ta kasar ta yi wani sharhi inda aka yabawa gwamnatin kasar Sin tana da aminci, kuma an nuna maraba ga ziyarar shugaba Hu Jintao.
Wannan sharhi mai lakabi "kasar Sin tana da aminci" ya ce, kasar Sin abokiya ce ta kasar Namibiya da duk kasashen Afirka. A watan Nuwamba na shekarar 2006, gwamnatin kasar Sin ta yi al'kawarin taimaka kasashen Afrika a taron koli na dandalin hadin gwiwar tsakanin kasashen Sin da Afrika da aka yi a birnin Beijing, bayan lokacin kadan, shugaba Hu Jintao ya kai ziyara a kasashen Afrika, wannan ya nuna cewa kasar Sin tana da aminci.
Ran 30 ga wata, shugaba Hu Jintao ya tashi daga Beijing don kai ziyara a kasashe 8 na Afirka, a ran 5 ga watan Fabrairu zai sauka a kasar Namibiya.
|