Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-01-30 10:46:57    
Shugaban kasar Sin ya kama hanyarsa zuwa kasashen Afirka takwas don yin ziyarar aiki

cri
Bisa gayyatar da takwarorinsa na kasashen Kamaru da Liberia da Sudan da Zambia da Nambia da Afirka ta kudu da Mozambique da Seychells suka yi masa ne, a yau 30 ga wata, shugaban kasar Sin, Mr.Hu Jintao ya tashi daga birnin Beijing, kuma ya fara yin ziyarar aiki a kasashen nan takwas. Wannan fa ya kasance ziyara ta farko da shugaba Hu Jintao ya yi a wannan shekara, haka kuma wani muhimmin al'amari daban ne a wajen huldar da ke tsakanin Sin da Afirka bayan taron koli na dandalin hadin kan Sin da Afirka.

Wani jami'in diplomasiyya na Sin ya bayyana cewa, a wannan ziyarar da yake yi, shugaba Hu Jintao zai fi mai da hankali a kan tabbatar da nasarorin da aka samu a gun taron koli na Beijing, kuma ana imani da cewa, ziyarar za ta kara ingantawa da zurfafa zumuncin gargajiya a tsakanin Sin da wadannan kasashen Afirka, kuma za ta kara samar da fahimtar juna da amincewa da juna a tsakaninsu, za ta kuma ingiza hadin gwiwa a tsakaninsu a fannoni daban daban, za ta sa kaimi ga samun zaman lafiya da kwanciyar hankali na shiyyar.(Lubabatu)