Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-01-22 17:41:21    
Ma'aikatan Sin biyar da aka yi awon gada da su a Nijeriya sun iso birnin Beijing lami lafiya

cri

A ran 22 ga wata da yamma, Sinawa biyar masu aikin injiniya wadanda 'yan bingida suka yi awon gaba da su a kasar Nijeriya sun iso birnin Beijing lami lafiya.

Kong Quan, mai ba da taimako ga ministan harkokin waje na kasar Sin wanda ya je filin jirgin sama don maraba da su ya bayyana cewa, bayan da aka yi garkuwa da su, shugaba Hu Jintao da firayim minista Wen Jiabao da sauran shugabannin kasar Sin sun mai da hankali sosai kan lafiyar wadannan Sinawa biyar, kuma sun bukaci hukumomin da abin ya shafa da su nemi dabaru wajen ceton su da kuma tabbatar da lafiyarsu.

Ban da wannan kuma Mr. Kong ya ce, gwamnatin kasar Sin tana dora muhimmanci da kuma kare hakkin Sinawan da ke ketare bisa dokoki. A waje daya kuma, fuskantar halin zaman lafiya mai yamutse da kasashen duniya ke ciki, ana fatan Sinawan da ke ketare za su iya kara fahimtar tsaron kai da kuma kula da lafiyar kansu.(Kande Gao)