Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International Sunday    Apr 6th   2025   
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-01-22 09:41:29    
Ma'aikata 5 na kasar Sin sun dawo gida daga Nijeriya

cri

Bayan da suka yi kwanaki 2 suna hutawa kadan a ofishin jakadanci na kasar Sin a kasar Nijeriya, ma'aikata 5 da aka 'yantar da su sun tashi daga Lagos a ran 21 ga wata misalin da karfe 3 da yamma, bisa agogon wurin domin dawowarsu a kasar Sin.

Wadannan ma'aikata 5 sun sauka filin jirgin sama na Lagos ne daga birnin Abuja cikin jirgin sama a wannan rana misalin da karfe 8 da safe bisa agogon wurin, sun kuma dawo gida cikin wani jirgin sama na kamfanin zirga-zirgar jiragen sama na Southern na kasar Sin misalin na karfe 3 na yamma.

Karamin jakadan kasar Sin a Lagos Yuan Wenjin da babban darektan ofishin kamfanin zirga-zirgar jiragen sama na Southern na kasar Sin a Lagos Jiang Nan sun yi wa wadannan ma'aikata ban kwana a filin jirgin saman, inda Mr. Yuan ya yi musu jaje a madadin ofishin karamin jakadancin kasar Sin, kuma yana fatan za su sauka lafiya.(Tasallah)