Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2007-01-08 08:47:31    
Shugaban karamar kabilar Nijeriya ya amince da cewa za a saki Sinawan da aka yi garkuwa

cri

Wakilin rediyon kasar Sin dake birnin Lagos ya ruwaito mana labari cewa , a ran 7 ga watan nan wani jami'in da bai sanar da sunansa ba ya ce, shugaban wata karamar kabilar Emohua da ke jihar Rivers ta kasar Nijeriya ya bayyana cewa , zai ba da taimako ga ceton Sinnawa 5 da aka yi garkuwa da su kwanan baya , kuma ya amince da cewa , za a saki Sinawan cikin lafiya .

Wannan jami'in ya ce , shugaban ya bayyana cewa , zai yi amfani da matsayinsa don ba da taimako ga Kungiyar ceto ta musamman ta Ofishin Jakadancin Kasar Sin da gwamnatin Wurin da 'yan sanda don ceton sinawan 5 . Idan za a yi aikin ceton yadda ya kamata , to , nan gaba kadan za a saki wadannan sinawan .

Amma duk da haka wannan jami'in bai sanar da sunan shugaban karamar kabilar ba.(Ado)