Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-11-08 08:27:09    
Tsarin hadin gwiwar Sin da Afirka ya cancanci kasashen yammaci su yi koyi da shi, in ji shugaban Afirka ta kudu

cri
Shugaban kasar Afirka ta kudu, Thabo Mbeki, wanda ya zo kasar Sin don halartar taron koli na dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka da kuma yin ziyara a kasar Sin, ya bayyana cewa, ma iya cewa, sabuwar huldar abokantaka da ke tsakanin Sin da Afirka ta ba da 'sabon ma'auni' wajen kullawa da kuma bunkasa hulda da kasashe masu tasowa, wanda ya kamata kasashen yammacin duniya su yi koyi da shi.

A ran 7 ga wata, jaridar 'The Star' ta Afirka ta kudu ta buga wani rahoton da wakilinta ya aika mata daga birnin Beijing dangane da hirar da aka yi da shugaban kasar, inda Mr.Mbeki ya ce, hadin gwiwar da ke tsakanin Sin da Afirka ya kafu ne bisa tushen moriyar juna, kuma idan hadin gwiwar zai iya taimakawa wajen farfado da Afirka, to, lalle ne ya kamata kasashe masu ci gaba na yammacin duniya su yi la'akari da yin koyi da tsarin hadin gwiwar.(Lubabatu)