Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-11-07 14:26:31    
Wu Bangguo ya gana da shugabannin kasashe 4 na Afrika

cri
A ran 6 ga watan nan a nan birnin Beijing , Wu Bangguo , Shugaban Majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ya gana da shugabannin kasashe 4 na Afrika , wato shugaba Mubarak na kasar Masar da shugaba Boutiflika na kasar Algeria da shugaba Mbeki na kasar Afrika ta kudu da firayin minista Ramgoolam na kasar Mauritius .

Mr. Wu da shugabannin kasashen 4 sun nuna yabo sosai ga taron kolin Beijing kan dandalin hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da Afrika wanda aka rufe shi ba da dadewa ba . Gaba daya suna ganin cewa , taron koli na wannan karo ya sami nasara , kuma yana da muhimmanci sosai kuma yana da babbar ma'ana ga tarihin hadin gwiwar zumunci tsakanin Sin da Afrika . Sun kuma bayyana cewa , za su tabbatar da yarjejeniyoyin da aka cim mawa a gun taron kolin , kuma za su ciyar da yalwatuwar dangantakar tsarin musamman da sabbin abokai tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika . (Ado)