Ran 5 ga wata, Mr. Li Zhaoxing ministan harkokin waje na kasar Sin ya ce, kasar Sin za ta yi kokari tare da kasashen Afirka don shimfida da jeren ra'ayoyi iri daya da aka samu a dandalin hadin gwiwar kasashen Sin da Afirka.
A gun taron manema labaru da Mr. Li Zhaoxing da Mr. Seyoum Mesfin ministan harkokin waje na kasar Habasha da Mr. Ahmed Abul-Gheit ministan harkokin waje na kasar Masar suka jagora, Mr. Li Zhaoxing ya ce, nan gaban kasashen Sin da Afirka za su rika tuntuba a matsayin manyan jami'i kan fannin siyasa, kuma shimfida ra'ayoyin iri daya da aka samu a taron koli na Beijing kan fannin tattalin arziki, kuma kasar Sin za ta cigaba da goyon baya kamfannonin kasar Sin su shiga ayyukan gina kasashen Afirka, kuma kara shigowar kayayyakin kasashen Afirka. Game da al'adu, sa kaimi ga cudanyar da al'adu iri iri, gina wata duniya mai jituwa. Kuma za a kara daidaita a fannin bangarorin dabam daban, kiyaye moriyar kasashe masu tasowa.
|