Ran 2 ga wata, bisa labarin da muka samu daga hukumar yawon shakatawa na kasar Sin, an ce, yanzu kasar Sin ta riga ta yarda da kasashe 17 su zama wurare inda mutanenta su iya yin yawon shakatawa.
An ce, a shekarun baya, hadin gwiwar yawon shakatawa dake tsakanin kasashen Sin da Afirka ta yi ta bunkasuwa, yawan mutanen da suke tafiyar a tsakaninsu ya karu sosai. yanzu, kasar Sin ta riga ta yarda da kasashe 17 su zama wurare inda mutanenta su iya yin yawon shakatawa, a cikinsu akwai kasashen Masar, Afirka ta kudu, Morocco, Mauritius, Habasha, Tunisia, Zimbabwe, Kenya, Tanzania, Seychelles, Zambia inda an riga an fara tafiya da aikin sabis na yawon shakatawa; kuma za a fara tafiya da wannan aiki a kasar Uganda a ran 1 ga watan Jarairu na shekara mai zuwa.
|