Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-11-02 14:40:51    
An rufe taron manyan jami'ai na 5 kan Dandalin hadin gwiwar tsakanin kasar Sin da Afrika a Beijing

cri

Wakilin Rediyon kasar Sin ya ruwaito mana labari cewa , a ran 2 ga watan nan , An rufe taron manyan jami'ai na 5 kan Dandalin hadin gwiwar tsakanin kasar Sin da Afrika a nan birnin Beijing

Wei Jianguo , sakataren Kwamitin shirya taron kolin Dandalin hadin gwiwar tsakanin Sin da Afrika kuma mataimakin Ministan harkokin Ciniki na Kasar Sin da Nolana Ta-Ama , shugaban Kungiyar jakadun kasashen Afrika da ke kasar Sin kuma jakadan kasar Togo dake kasar sun yi jawabi a gun bikin rufe taron .

Mr. Wei ya bayyana cewa , a cikin shekaru 6 da suka shige , Bayan da aka kafa dandalin hadin gwiwar tsakanin Sin da Afrika , hadin gwiwar tsakaninsu a fannoni daban daban ya sami yalwatuwa da saurin gaske . A gun taron kolin Beijing , shugabannin kasar Sin da na Afrika za su musaya ra'ayoyinsu sosai kan yadda za a kara bunkasa huldar dake tsakaninsu. Taron tabbas ne zai kara sabon karfi kan zumunci da hadin gwiwa dake tsakanin Sin da Afrika .

Mr. Ta Ama ya ce , wannan shekara cikon shekaru 50 ne da kasar Sin da kasashen Afrika suka kulla huldar diflomasiya . Taron kolin Beijing kan Dandalin hadin gwiwar tsakanin Sin da Afrika zai zama muhimmin batu a tarihin dangantakar tsakanin Sin da Afrika , kuma tabbas ne zai kara karfafa huldar dake tsakaninsu da ba da taimako ga karfafa zumunci da inganta hadin gwiwa da samun bunkasuwa tare . (Ado)