Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-10-20 11:17:07    
Manoma fiye da 7000 na Baoding na Hebei na kasar Sin suna aiki a kasashen Afrika

cri
Wakilin Kamfanin dillancin labarum Xinhua na kasar Sin ya ruwaito mana labari cewa , tun daga shekarar 1999 , manoman Birnin Baoding na Lardin Hebei na kasar Sin suka fara zuwa kasashen Afrika don samun aikin yi . A cikin shekaru 7 da suka shige, yawan manoman da suke aikin noma da kasuwanci da ciniki a kasashen Afrika ya riga ya kai fiye da 7000 .

Bisa bayanin da aka yi , an ce , lokacin da manoman birnin Baoding suke noman kayan lambu da shinkafa da alkama da masar, wasu daga cikinsu kuma 'yan kasuwa ne, yayin da wasu kuma suna aikin gyare-gayren na'urori . Yanzu sun riga sun kafa Kauyen Baoding 28 a kasar Zambia da Kenya da Habasha da sauran kasashe 14 na Afrika .

Bisa labarin da aka bayar , an ce, gwamnatocin kasashen Afrika suna maraba da Kauyen Baoding , saboda manoman kasar Sin sun samu na'urori da fasahohi na zamani kuma sun samar da abinci da wadatuwa ga Afrikawa. (Ado)