Ran 19 ga wata da safe a birnin Xiamen na lardin Fujian na kasar Sin, an bude taron nuna kayayyakin aikin gona da taron gabata da ayyuka na hadin gwiwar tsakanin gabobi biyu na zirin Taiwan. Madam Wu Yi mataimakiyar firaministan majalisar gudanarwa kuma 'yar ofishin siyasa na jam'iyyar kwaminis ta tsakiya ta kasar Sin, da Mr. Lianzhan shugaba mai girma na jam'iyyar Kwamintang sun harlarci bikin bude taron.
Ofishin kula da harkokin Taiwan na jam'iyyar kwaminis ta tsakiya ta kasar Sin da hukumomin jam'iyyar Kwamintang sun jagorar da wannan taro, wannan wani kashi mai muhimmanci na dandalin hadin gwiwar aikin gona na gabobi biyu na zirin Taiwan. Abubuwan da ke cikin wannan taron su kunshe da nuna kayayyakin aikin gona na hadin gwiwa tsakanin gabobin biyu, bikin sa hannu na hadin gwiwar aikin gona, gabatar da ayyuakn zuba jari.
|