Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-09-19 08:45:41    
Kasar Nijeriya ta soma zaman makoki saboda manyan hafsoshin da suka rasu a cikin hadarin faduwar jirgin sama

cri
A ran 18 ga wata, shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya sanar da cewa, an soma zaman makoki har na tsawon kwanaki 3 saboda mutuwar manyan jami'ai 12 a cikin hadarin jirgin sama da ya auku a ran 17 ga wata.

A wannan rana, madam Oluremi Oyo, mai ba da taimako ga shugaban kasar Nijeriya kan harkokin watsa labaru da kafofin watsa labaru, ta bayyana cewa, bayan da shugaba Obasanjo wanda ke yin ziyara a kasar Singapore ya sami labarin aukuwar hadarin faduwar jirgin sama, ya nuna bakin ciki da mamaki sosai. Madam Oyo ta tsamo maganar Obasanjo tana, cewar hadarin faduwar jirgin sama "wata babbar masiffa ce ga duk kasar Nijeriya". Madam Oyo ta kara da cewa, shugaba Olusegun Obasanjo ya riga ya gama ziyararsa a kasar Singapore ya koma kasarsa kafin lokacin da aka tsara.

Bugu da kari kuma, Mr. Obasanjo ya nuna jejeto ga iyalan hafsohin da suka rasu a cikin hadari, ya kuma ba da umurnin binciken dalilin da ya haddasa wannan hadari nan da nan. (Sanusi Chen)