A ran 18 ga wata, shugaban kasar Iran Mahumd Ahmadinejad, wanda yake ziyarar aiki a kasar Venezuela, ya bayyana cewa, kamata ya yi kasar Amurka ta canza matakai da take dauka, idan ta yi haka, to, za a iya daidaita matsalolin da ake fuskanta ciki har da matsalar nukiliya.
Mr Ahmadinejad ya karfafa cewa, kasar Amurka ta yanke huldar da ke tsakaninta da kasar Iran, sabo da haka, idan gwamnatin kasar Amurka tana son maido da huldar da ke tsakaninta da kasar Iran, to, kamata ya yi ta dauki matakai bisa son rai. A sa'i daya kuma ya ce, jama'ar kasar Amurka suna neman zaman lafiya da aminci da adalci.(Danladi)
|