Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-09-15 18:08:29    
Gwamnatin kasar Sin ta kebe kudi da yawa domin ayyukan ba da agaji

cri
Bisa labarin da kamfanin dillancin labaru na Xin Hua ya bayar, an ce, ya zuwa yanzu, gwamnatin tsakiya ta kasar Sin ta riga ta kebe kudin Renminbi yuan kimanin biliyan 7 da miliyan dari 1 daga baitulmali domin ayyukan ba da agaji da ayyukan sake neman bunkasuwa a lardunan Hunan da Fujian da Guangdong da Guangxi kuma da lardin Sichuan wadanda suka sha fama da bala'u daga indallahi.

Ma'aikatar kudi ta kasar Sin ta bayar da wannan labari a ran 15 ga wata.

An bayar da labari cewa, yanzu, muhimman ayyukan ba da agaji a wurare da suka sha fama da bala'u daga indallahi sun hada da inganta rayuwar jama'a da sake masu gidajen kwana.

Kwanan baya, ma'aikatar kula da harkokin jama'a ta kasar ta bayyana cewa, za a tabbatar da magance matsalar rashin wurin kwana ga wadanda bala'u suka rutsa da su kafin lokacin hunturu. A watan Nuwamba mai zuwa, hukumomin da abin ya shafa za su yi kira ga al'ummar kasar da su ba da taimakon kudi da kayayyaki ga mutanen da ke sha fama da bala'u. (Sanusi Chen)