Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-09-05 19:32:08    
Sakamakon da kasar Sin ta samu daga yin hadin gwiwa da kungiyoyin duniya wajen shawo kan murar tsuntsaye ta sami amincewa daga kasashen duniya

cri
Ran 5 ga wata, mataimakin shugaban hukumar likitocin dabbobi ta ma'aikatar aikin noma ta kasar Sin Mr. Li Jinxiang ya bayyana cewa, ma'aikatar aikin noma ta kasar Sin ta hada gwiwa sosai da kungiyoyin kasa da kasa da ma'aikatan kiwon lafiya na kasashen da abin ya shafa wajen shawo kan annobar murar tsuntsaye, sun yi musayar bayanai yadda ya kamata, sakamakon da ta samu ya sami amincewa daga kasashen duniya.

A gun taron ganawa da manema labaru da aka yi a nan Beijing, Mr. Li ya yi bayanin cewa, ma'aikatar aikin noma ta kasar Sin ta sanar da kungiyoyin kasa da kasa da kasashen da abin ya shafa kan halin da take ciki a sakamakon barkewar annobar murar tsuntsaye a kasar, da kuma sakamakon sa ido da bincike da kuma yadda ta daidaita barkewar wannan annoba.(Tasallah)