Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-09-05 16:59:00    
Firayin ministan kasar Jordan ya kai suka bisa bude wutar da aka yi wa 'yan yawon shakatawa na kasashen waje

cri

A ran 4 ga wata, firayin ministan kasar Jordan Marouf Bakhet ya kai suka bisa bude wutar da aka yi wa 'yan yawon shakatawa na kasashen waje a ran nan da safe.

Mr Bakhet ya ce, wannan mataki da aka dauka yana barazana ga zaman lafiyar kasar Jordan, kuma ya harzuga jama'ar kasar Jordan.

Ya ci gaba da cewa, a halin yanzu hukumomin da abin ya shafa suna bincike a kan wannan lamari, ya yi imani cewa, za a gano ko wane ne ke hannu a cikin wannan danyen aiki.

Bisa labarin da muka samu, an ce, a ran 4 ga wata a wurin da ke dab da tsohon dakin wasannin kwayikwayo a birnin Amman, wani 'dan kasar Jordan ya bude wuta ga wata tawagar 'yan yawon shakatawa na kasashen waje, wannan ya sa wani 'dan yawon shakatawa na Britaniya ya mutu tare da sauran 'yan yawon shakatawa 5 da wani 'dan sanda suka ji rauni.

Kakakin gwamnatin kasar Jordan Hanna Nasser ya bayyana cewa, bude wutar da aka yi wa 'yan yawon shakatawa na kasashen waje a ran 4 ga wata a birnin Amman, babban birnin kasar Jordan, ba shi da nasaba da ko wace kungiya ko dakaru.(Danladi)