Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-09-03 21:22:47    
Togo ta dora muhimmanci kan daidaita matsalar samun aikin yi da matasa ke fama da ita

cri
Ran 2 ga wata, a birnin Lome, hedkwatar kasar Togo, lokacin da yake zantawa da manema labaru, ministan kula da horar da matasa na kasar Mr. Gilbert Kodjo Atsu ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Togo ta dora muhimmanci kan batun matasa, ta mayar da aikin warware mastalar samun aikin yi da matasa ke fama da ita a gaban kome, ta kuma sami sakamako.

Mr. Atsu ya kara da cewa, matasa muhimmin kashi ne da ke cikin al'ummar kasar Togo. Saboda haka, yau da misalin shekara 1 da ta gabata, gwamnatin kasar ta kafa ofishin minista da ke kula da horar da matasa.

Ya ci gaba da cewa, samun aikin yi na daya daga cikin manyan batutuwan da matasan kasar Togo ke fuskanta a yanzu, shi ya sa gwamnatin kasar ta tsai da kudurin ba da taimako gare su wajen samun aikin yi ta hanyar tsara shirye-shirye kan horar da su da kuma tsugunar da su.(Tasallah)