Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-09-02 21:23:57    
Mutane 4 sun mutu ko sun jikata a sakamakon fashewar motar kungiyar Red Cross a Senegal

cri
Kafofin yada labaru na kasar Senegal sun ba da labari a ran 2 ga wata cewa, an samu fashewar wata mota ta kungiyar agaji ta Red Cross ta kasa da kasa a lardin Casamance da ke kudancin kasar Senegal a ran 1 ga wata da yamma, inda mutum daya ya rasa ransa, yayin da wasu 3 suka ji rauni.

Kakakin kungiyar agaji ta Red Cross ta kasa da kasa ya bayyana cewa, yanzu kungiyar tana binciken asalin mutumin da ya mutu da wadanda suka jikata. Ya kuma tabbatar da cewa, an samu wannan fashewar mota a wurin da ke da nisan kilomita misalin 100 a tsakaninsa da birnin Ziguinchor, babban birnin lardin Casamance a kudancin kasar Senegal, amma ya zuwa yanzu ba a san dalilin da ya haddasa wannan fashewa ba tukuna.(Tasallah)