Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-08-30 21:39:41    
EU za ta samar wa Lebanon kudin Euro miliyan 42 domin farfado da kasar

cri
A ran 30 ga wata, kwamitin kungiyar Tarayyar Turai ya sanar da cewa, kungiyar Tarayyar Turai, wato EU za ta samar wa kasar Lebanon taimakon kudin da zai kai kudin Euro miliyan 42 domin sake gina kasar. Sakamakon haka, ya zuwa yanzu, bayan kawo karshen wutar yaki a tsakanin Isra'ila da Lebanon, jimlar kudin taimakon da kungiyar Tarayyar Turai ta samar wa Lebanon ta riga ta kai fiye da kudin Euro miliyan dari 1.

Benita Ferrrero-Waldner, wakiliyar kungiyar Tarayyar Turai wadda ke kula da aikin tsara manufofin diplomasiyya da na neman jituwa a tsakanin kasashen da suke makwabtaka da juna ta bayyana cewa, muhimmiyar nasarar da za a ci wajen sake raya kasar Lebanon ita ce gwamnatin Lebanon ta zama wata gwamnatin da take da cikakken ikon mulkin kasar cikin 'yanci. Sa'an nan kuma, dole ne a aiwatar da yarjejeniya mai lamba 1701 ta kwamitin sulhu na M.D.D. yadda ya kamata. (Sanusi Chen)