Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-08-26 16:51:08    
Kasashen Sin da Kazakhstan sun yi atisayen hadin guiwarsu na zagaye na biyu don yaki da ta'addanci a jihar Xinjiang ta kasar Sin

cri
Ran 26 ga wata da safe, kasar Sin ta yi atisaye mai lambar Tianshan ?1 a birnin Yining na jihar Xinjiang da ke arewa maso yammacin kasar Sin, wato atisayen hadin guiwa na zagaye na biyu da ake yi a tsakanin kasashen Sin da Kazakhstan don yaki da ta'addanci.

A lokacin da ake yin wannan atisaye, kasar Sin ta yi amfani da jiragen saman yaki masu saukar ungulu da motocin yaki masu kwantar da tarzoma da sauran makamai. A cikin atisayen da aka shafe sa'o'I biyu da wasu mintoci ana yinsa, sojoji masu yaki da ta'addanci sun yi kazamin fada da 'yan ta'adda, kuma sun hallaka su kwata-kwata. 'Yan kallo sama da 100 wadanda suka fito daga kasar Sin da sauran kasashe na kungiyar hadin kai ta Shanghai suna wurin atisayen. (Halilu)