A ran 23 ga wata da dare, wani jami'in gwamnatin Nijeriya ya bayyana cewa, an riga an saki dukkan ma'aikata 6 ma'aikatan man fetur wadanda aka tsare su a mashigar ruwa ta Port Harcourt da ke kudancin kasar Nijeriya.
Magnus Abe, kakakin gwamnatin jihar Rivers ta Nijeriya ya bayyana cewa, daga cikin wadannan ma'aikata 6 ma'aikatan man fetur da aka tsare su har da Amurkawa 2, da mutane 2 na Ingila, da mutum daya na kasar Poland, dayan na Ireland, dayan kuma na Faransa. Amma bai fayyace wadannan mutane su wane ne ba.
An ce, wandannan mutane baki da aka sake su an sace su ne a ran 13 ga wata da dare a wata mashayar giya da ke mashigar ruwa ta Port Harcourt. (Umaru)
|