Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-08-21 21:20:45    
Kasar Iran za ta ci gaba da shirinta na makamashin nukiliya

cri

A ran 21 ga wata a birnin Tehran, shugaban addini na kasar Iran Ali Khamenei ya bayyana cewa, kasar Iran za ta ci gaba da shirinta na makamashin nukiliya.

A ran nan Mr Khamenei ya yi wani jawabi a gidan TV na kasar Iran cewa, kasar Iran za ta ci gaba da gudanar da shirinta na amfani da makamashin nukiliya.

A ran nan a birnin Pretoria na kasar Afirka ta kudu, ministan harkokin waje na kasar Iran Manouchehr Mottaki, wanda yake ziyarar aiki a kasar, ya bayyana cewa, kasar Iran ta riga ta shirya sosai domin ba da amsa ga shirin da ministocin harkokin waje 6 suka gabatar. Ya ci gaba da cewa, Iran tana fata za a warwae matsalar nukiliya ta kasar Iran ta hanyar yin shawarwari, kamata ya yi a giramama ikon da kasar Iran take da shi wajen amfani da makamashin nukiliya.(Danladi)