Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International Sunday    Apr 6th   2025   
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-08-21 10:37:42    
Kasashen Larabawa sun yi alkawarin ba da taimako ga kasar Lebanon don farfado da kasar bayan rikicin Lebanon da Isra'ila

cri

Wakilin Rediyon kasar Sin ya ruwaito mana labari cewa , a ran 20 ga watan nan a birnin Alkahira , hedkwatar kasar Masar , ministocin harkokin waje da wakilan kasashen Larabawa sun yi taro , inda suka yi alkawarin ba da taimako ga kasar Lebanon don farfado da kasar .

A wannan rana ministocin da wakilan kasashe mambobi 22 na Kungiyar tarayyar kasashen Larabawa sun halarci taron kan matsalar Lebanon . Mahalartan taron sun yi na'am da kai gundumuwa ga kasar Lebanon wadda kasar Isra'ila ta kaiwa farmaki sau da yawa a yankin . Za a sanar da hakikanin shirin kai agaji a taron ministocin kudi na kasashen Larabawa a watan Satumba .

Mahalartan sun kuma bayar da sanarwa , inda suka la'anci kasar Isra'ila saboda ta taka kuduri mai lambar 1701 na Kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya zartas a ran 19 ga watan Agusta . (Ado)

© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China. 100040