Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International Sunday    Apr 6th   2025   
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-08-02 11:53:19    
Yaki tsakanin kasar Isra'ila da kasar Lebanon yana ci gaba Kungiyar tarayyar Turai ta yi kira da su sasauta

cri

Wakilin Rediyon kasar Sin ya aiko mana labari cewa , a ran 1 ga watan nan , Yaki tsakanin kasar Isra'ila da Kungiyar Hezbollah ta kasar Lebanon yana ci gaba . Bangarorin biyu sun sami rauni da mutuwa. A wannan rana , ministocin harkokin waje na Kungiyar tarayyar Turai sun yi taron musamman , inda suka yi kira ga banrarorin biyu da su sasauta.

A ran 1 ga watan sojojin Isra'ila da dakaru masu dauke da makamai na Kungiyar Hezbollah sun yi musayar wutar yaki a wani Kauyen dake iyakar kudancin kasar Lebanon , ya yi sanadiyyar mutuwar sojoji 3 na kasar Isra'ila . Sauran sojoji 25 sun ji rauni .

A wannan rana Kungiyar tarayyar Turai ta yi taron musamman a birnin Brusel , kuma ta bayar da sanarwa , inda ta yi kira ga bangarorin biyu da su yi shirin tsagaita bude wuta cikin dogon lokaci . Erkki Tuomioja , ministan harkokin waje na kasar Finland , kasar shugaban Kungiyar tarayyar Turai ya jaddada cewa , ya kamata Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ta dauki matakin gaggawa don hana yaduwar yakin tsakanin bangarorin biyu . A shirye suke kasashen Turai su shiga aikin kiyaye zaman lafiya . (Ado)

© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China. 100040