Sin ciki da waje (chinaabc)Rediyon kasar SinSashen Hausa
China Radio International
Labarun gida
Labarun duniya
Labarun Siyasa
Labarun Tattalin Arziki
Labarun Al'adu
Labarun Wasanni
Sauran Labaru
Saurari labarai da dumi-duminsu da sauran shirye-shirye
more>>
[ Al'adu ]
 --Al'adun Sinawa
 --Kabilun kasar Sin
[ Bunkasuwa ]
 --Tattalin arziki
 --Bunkasuwar Sin
[ Yawon shakatawa ]
 --Yawo a kasar Sin
 --Wurare masu yawo
[ Ilmi, Lafiya ]
 --Fagen bincike
 --Kiwon lafiya
[ Wasanni ]
 --Labaran wasannin
 --Me ka sani
(GMT+08:00) 2006-08-02 11:53:19    
Yaki tsakanin kasar Isra'ila da kasar Lebanon yana ci gaba Kungiyar tarayyar Turai ta yi kira da su sasauta

cri

Wakilin Rediyon kasar Sin ya aiko mana labari cewa , a ran 1 ga watan nan , Yaki tsakanin kasar Isra'ila da Kungiyar Hezbollah ta kasar Lebanon yana ci gaba . Bangarorin biyu sun sami rauni da mutuwa. A wannan rana , ministocin harkokin waje na Kungiyar tarayyar Turai sun yi taron musamman , inda suka yi kira ga banrarorin biyu da su sasauta.

A ran 1 ga watan sojojin Isra'ila da dakaru masu dauke da makamai na Kungiyar Hezbollah sun yi musayar wutar yaki a wani Kauyen dake iyakar kudancin kasar Lebanon , ya yi sanadiyyar mutuwar sojoji 3 na kasar Isra'ila . Sauran sojoji 25 sun ji rauni .

A wannan rana Kungiyar tarayyar Turai ta yi taron musamman a birnin Brusel , kuma ta bayar da sanarwa , inda ta yi kira ga bangarorin biyu da su yi shirin tsagaita bude wuta cikin dogon lokaci . Erkki Tuomioja , ministan harkokin waje na kasar Finland , kasar shugaban Kungiyar tarayyar Turai ya jaddada cewa , ya kamata Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ta dauki matakin gaggawa don hana yaduwar yakin tsakanin bangarorin biyu . A shirye suke kasashen Turai su shiga aikin kiyaye zaman lafiya . (Ado)